DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kudurin kayyade shekarun ’yan takarar Shugaban kasa da Gwamna ya tsallake karatu na biyu

-

Majalisar wakilai

Majalisar Wakilai ta amince da kudurin da ke neman kayyade shekarun masu neman kujerar shugaban kasa da na gwamna zuwa karancin shekaru 60, yayin da kudirin ya tsallake karatu na biyu a zauren majalisar.

Kudurin wanda dan majalisa Ikeagwuonu Ugochinyere, mai wakiltar mazabar Ideato ta Arewa daga jihar Imo, ya gabatar, yana neman a gyara sashe na 131 da na 179 na kundin tsarin mulkin Nijeriya.

A cewar Ugochinyere, ya kamata a sabunta tsarin ne domin bai wa sabbin jini damar shiga tafiyar siyasa, tare da tabbatar da cewa wadanda ke rike da manyan mukamai na kasa suna da kuzari da sabbin dabaru.

Yanzu haka, kudurin na jiran ci gaba da tattaunawa da nazari a matakai na gaba kafin ya kai ga zama doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Atiku Abubakar ya caccaki hukumar EFCC kan tsare tsohon dan majalisa Gudaji Kazaure

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya soki hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, kan tsare tsohon dan...

Gwamnatocin Pakistan da Indiya sun amince da tsagaita wuta a Asabar dinnan

Ministan harkokin wajen Pakistan Ishaq Dar ya sanar a shafinsa na X cewa, kasashen sun amince da Shirin tsagaita wuta cikin gaggawa. Shugaba Trump ya sanar...

Mafi Shahara