DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kasashen AES sun janye Jakadunsu daga Aljeriya bayan zargin kakkabo jirgin Mali

-

Mali/Nijar/Burikina Faso

Kasashen kungiyar AES sun janye jakadunsu daga kasar Aljeriya, bayan zargin da kasar Mali ta yi cewa Aljeriya ta harbo mata jirgin yaki marar matuki a ranar 31 ga Maris zuwa safiyar 1 ga Afrilu.  

A cewar sanarwar da gwamnatin Mali ta fitar, an harbo jirgin mai kirar TZ-98D a yankin Tin-Zaouatène da ke jihar Kidal, kusa da iyakar Aljeriya.

Gwamnatin Mali ta zargi Aljeriya da keta huruminta da kuma amfani da makami mai linzami wajen kakkabo jirgin. 

Sai dai daga bisani, Aljeriya ta bayyana a kafafen yada labaranta cewa ta kakkabo wani jirgi da ya shige sararinta da kusan kilomita biyu, zargin da Mali ta musanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cin hanci la’ana ce, mu tsabtace kanmu daga rashawa- EFCC

A wani sakon tunatarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook albarkacin ranar Juma’a, hukumar da ke yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya,...

Babu karar-kwana, da tuni na bakuncin lahira a zanga-zangar #EndSARS – Jarumi a Nollywoood Desmond Elliot

Fitaccen ɗan wasan fina-finan Nollywood kuma ɗan siyasa, Hon. Desmond Elliot, ya bayyana yadda ya kuɓuta daga wani hari da wasu baƙin fuska suka yi...

Mafi Shahara