DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sudan ta kauracewa taron Birtaniya kan rikicin kasarta

-

 

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sudan ta bayyana rashin amincewarta da kuma kauracewa wani babban taro da Birtaniya ke shirin gudanarwa a tsakiyar watan Afrilu a birnin London, wanda zai tattauna rikicin Sudan.  

A cikin wata wasika da ya aikewa Sakataren Harkokin Wajen Birtaniya, David Lammy, Ministan Harkokin Wajen Sudan, Ali Yousif, ya soki matakin Birtaniya na gayyatar wasu kasashe kamar UAE, Chadi da Kenya, wadanda Sudan ke zargi da marawa dakarun Rapid Support Forces (RSF) baya.  

Taron dai na gudana ne tare da hadin gwiwar Tarayyar Turai (EU), Faransa, da Jamus, da nufin lalubo mafita kan rikicin da ya dabaibaye kasar Sudan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ba gasa muke yi da kamfanin NNPCL ba – Dangote

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, alhaji Aliko Dangote, ya bayyana cewa matatar man fetur dinsa ba ta yin gasa da Kamfanin man Fetur na Nijeriya, wato...

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun kama wasu ‘yan jarida uku na Radio Sahara da ke jihar Agadez

Rahotanni daga gidan Radio Sahara Fm da ke jihar Agadez sun tabbatar da kama wasu 'yan jaridar gidan radiyon guda uku da suka hada da...

Mafi Shahara