DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya yi abin a zo a yaba da ya nada kwararre a shugabancin asusun harkokin noma – Umar Abdullahi Yaya

-

An bayyana nadin Muhammed Abu Ibrahim a matsayin shugaban asusun kula da ci gaban harkokin noma da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi a matsayin abinda ya dace, wanda zai samar da ci gaba a fannin noman ƙasar nan.
Sakataren kungiyar masu kiwon kaji na jihar
Katsina, Alhaji Umar Abdullahi Yaya, ne ya bayyana hakan ya yin hira da yan jarida a Katsina.
 
Ya ce wanda aka naɗan, kwararren Akaunta ne, wanda ke da kwarewa kan shugabanci na sama da shekaru 25 a bangarorin harkokin kudi da fasaha da aikin gona.
Umar Yaya ya ce Mr Ibrahim shi ne wanda ya kafa wata cibiya mai suna (Sponge Analytics); wacce ka tattara bayanai kan harkokin noma da samar da mafita.
Malam Ibrahim wanda kafin nadin nasa shi ne mataimakin shugaban cibiyar (Livestock247); cibiyar harkoki da ci gaban dabbobi, irinta na farko a Najeriya.
 
Hakazalika, Ibrahim ya kasance memba a kwamitotin zartarwa na kampanoni da dama da suka shafi fasaha da muhalli da aikin gona da sai sauransu.
Alhaji Umar Yaya ya bayyana nadin a matsayin wanda yazo a kan lokaci, kuma mai karfafa gwiwar matasan ƙasar nan baki ɗaya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a...

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Mafi Shahara