Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedBabu wanda ya yi barazanar tsige Akpabio daga mukaminsa - Majalisa

Babu wanda ya yi barazanar tsige Akpabio daga mukaminsa – Majalisa

Majalisar dokokin Nijeriya ta sa kafa ta shure wasu rahotannin da ake yadawa a kafafen watsa labarai cewa wasu fusatattun ‘yan Sanatoci na shirin tsige shugabansu Sanata Godswill Akpabio.
Akwai wasu rahotannin da kafafen yada labarai suka watsa a ranar Asabar cewa ana shirin tsige shugaban majalisar dattawan Nijeriya Sanata Godswill Akpabio.
Rahotonannin sun ce akwai wasu Sanatoci da suka yi wata ganawa ta musamman a kasar Saudi Arabia don su kitsa yadda za a tsige Akpabio.
Sai dai, mai magana da yawun majalisar Yemi Adaramodu a cikin wata sanarwa a ranar Asabar, ya bayyana wadannan rahotannin da cewa ba su da tushe bare makama.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata