Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedMatashi ya kashe mahaifinsa don yin tsafin da zai kudance

Matashi ya kashe mahaifinsa don yin tsafin da zai kudance

Wani matashi mai suna Ridwan dan kimanin shekaru 20 a duniya ya hallaka mahaifinsa domin ya yi tsafin da zai sa ya samu kudi a jihar Ogun.
Kungiyar ‘yan sintirin jihar Ogun dai ne suka yi nasarar kama matashin a yankin Ijebu ta arewa a jihar. Kwamandan sintirin Soji Ganzallo a cikin wata sanarwa ya ce jami’ansa ne suka yi nasara kama matashin a lokacin da suke aikin sintiri, sai suka ji hayaniyar mutane a cikin wani kango.
Ganzallo ya ce da jami’ansa suka kutsa kai cikin gini, sai suka tarar da mutum sharbe cikin jini, wanda ake zargin ya yi aika-aikar ya tsere.
Kwamandan ya ce nan take ya ba jami’ansa umurnin su kamo wanda ake zargin cikin sa’o’i 24, kuma haka aka yi, suka nemo shi a inda ya ke labe a cikin daji.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata