Monday, April 6, 2026
HomeUncategorized"Za mu kara albashin ma'aikatan Shari'a don yaki da rashawa" - Tinubu

“Za mu kara albashin ma’aikatan Shari’a don yaki da rashawa” – Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi alkawari cewa gwamnatinsa za ta yi wa ma’aikatan Shari’a karin albashi da ma sanya masu alawus-alawus ta yadda za a magance matsalolin cin hanci da rashawa a fannin Shari’a.
Shugaba Tinubu ya yi wannan alkawarin ne yayin da ya karbi bakuncin shugabannin kungiyar lauyoyin Nijeriya (NBA) a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
A cewar sanarwar shugqban ya ce sun lura cewa ya zama tilas gwamnati ta yi yaki da cin hanci da rashawa don haka za su yi nazari sosai kan albashi da alawus-alawus na jami’an shari’a”.
Tawagar NBA ta samu jagorancin shugaban kungiyar, Yakubu Maikyau, babban lauyan Nijeriya (SAN), mai magana da yawun shugaban kasa, Ajuri Ngelale.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata