Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedBa Turawan Yamma ke ingiza mu daukar mataki kan Nijar ba -...

Ba Turawan Yamma ke ingiza mu daukar mataki kan Nijar ba – ECOWAS

Kungiyar ECOWAS ya musanta rade-radin da ake yi cewa Turawan Yamma ne ke juya akalarta game da rikicin juyin mulkin Nijar.
Shugaban hukumar kungiyar ta ECOWAS Omar Aleiu Touray ne ya sanar da hakan a Abuja a lokacin da ya kira taron manema labarai.
A ranar 26 ga Julin 2023 ne dai sojoji suka hambarar da gwamnatin farar hula ta Bazoum a Nijar, inda sojojin suka nada Janar Abdourahamane Tchiani a matsayin shugaba na riko.
Kungiyar ECOWAS dai ta sha sukar lamirin sojojin da suka yi wannan juyin mulkin, inda suka saka wa Nijar dokoki daban-daban da zummar sojojin su ji matsi su mayar da gwamnatin farar hula a kasar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata