DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya ta ji kunya a idon duniya – Obasanjo

-

Tsohon shugaban kasar Nijeriya Olusegun Obasanjo ya ce shekaru 63 da samun ‘yancin kan kasar, har yanzu ba ta yi wani abin a zo a gani ba.
Obasanjo na magana ne a Abuja wajen kaddamar da littafin da tsohon ministan ciniki da masana’antu Olusegun Aganga ya rubuta.
Ya ce a lokacin da kasar ta samu ‘yancin kai, ta zamo wata tauraruwa mai haske. Ya ce idan ana son gyara kasar, dole ne sai shugabanni sun amsa laifin cewa akwai matsala.
“Mun ji kunya, mun sa nahiyar Afrika ta ji kunya, mun sa bakaken fata sun ji kunya sannan mun ji kunya a idon duniya”. In ji Obasanjo.
Tsohon shugaban kasar ya ce kasar ba ta ajiye kowace kwarya a gurbinta. Ya ce son zuciya ya dabaibaye kowa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara