DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi ya bayyana shirin gwamnatinsa na yi wa makiyaya rijista a jihar sakamakon karuwar kwararar makiyaya daga jamhuriyar Nijar zuwa Jigawa

-

Malam Umar Namadi

Gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi ya bayyana shirin gwamnatinsa na yi wa makiyaya rijista a jihar sakamakon karuwar kwararar makiyaya daga jamhuriyar Nijar zuwa Jigawa 

Gwamna Namadi ya bayyana damuwar sa kan yadda ake samun karuwar mace-mace da raunata mutane da rakuma wadanda suka fito daga jamhuriyar Nijar, yayin da suke tsallaka manyan tituna a jihar.

Jihar Jigawa,na daya daga cikin jihohin Arewa maso Yammacin kasar da ke makwabtaka da jamhuriyar Nijar, kasar da ta shahara wajen kiwon rakuma, da a yanzu haka ke samun  yawaitar hadurran da ke da alaka da rakuma akan hanyoyin ta.

An bayyana cewa, rakuma wadanda suka saba kiwo da dare, suna tsallaka kan iyaka daga kasar Nijar zuwa cikin Nijeriya, suna yawo a sassan jihar Jigawa lamarin da ke haddasa hadurra da dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Atiku Abubakar ya caccaki hukumar EFCC kan tsare tsohon dan majalisa Gudaji Kazaure

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya soki hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, kan tsare tsohon dan...

Gwamnatocin Pakistan da Indiya sun amince da tsagaita wuta a Asabar dinnan

Ministan harkokin wajen Pakistan Ishaq Dar ya sanar a shafinsa na X cewa, kasashen sun amince da Shirin tsagaita wuta cikin gaggawa. Shugaba Trump ya sanar...

Mafi Shahara