DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministan Ilimi Tunji Alausa, ya bukaci majalisar dokokin Nijeriya ta dakatar da aiki kan kudirin kafa sabbin jami’o’i

-

Tunji Alausa

Ministan Ilimi Tunji Alausa, ya bukaci majalisar dokokin Nijeriya ta dakatar da aiki kan kudirin kafa sabbin jami’o’i

Da yake jawabi a wajen taron manema lanarai na ministoci da aka yi a Abuja, Tunji Alausa ya koka da yadda jami’o’i ke kara yawa yayin da wadanda ake da su ke fama da kalubalen kudade.

Google search engine

Ministan ya yi kira ga ‘yan majalisar tarayyar, da su dakatar da kudurin kafa sabbin jami’oin domin suna cin kudade da yawa, inda ya ce zuwa yanzu akwai kudirori kusan 200 a gaban majalisar dokokin kasar na kirkiro sabbin jami’o’i, kuma wadanda ake da su babu isassun kayan aikin tafiyar da su.

Don haka ya bukaci maimakon kafa sabbin makarantu, kamata ya yi a inganta wadanda ake da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tinubu ya gargadi Alkalan Nijeriya da kada su karkata ga cin hanci ko rashin adalci

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga alkalai da sauran ma’aikatan shari’a a Najeriya da su ci gaba da zama masu gaskiya, adalci,...

PDP ta musanta zargin kirƙirar sa hannun Sakataren ta na kasa

Kwamitin zartaswa na Ƙasa na jam’iyyar PDP ya musanta zargin ƙirƙirar sa hannu da Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, ya yi. Mai magana da...

Mafi Shahara