DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Abba a Kano ta haramta gabatar da shirin siyasa kai tsaye a kafafen yada labarai

-

Gwamnatin jihar Kano ta haramta gabatar da shirye-shiryen siyasa kai tsaye a gidajen rediyo da talabijin, jihar. Hakan na a matsayin wani matakin da ta ce ta dauka don kare tarbiyya da kuma dakile yaduwar kalaman da ka iya tunzura jama’a.

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar, Ibrahim Abdullahi Waiya, ne ya sanar da hakan yayin wata ganawa da shugabannin kafafen yada labarai, inda ya jaddada bukatar bin ka’idojin aikin jarida da ke girmama dabi’u da addinin al’ummar jihar.

Google search engine

A cewar Waiya, wannan haramcin ba wata hanya bace ta danne ra’ayoyin siyasa, illa dai dabarar hana yada kalaman tunzuri ko batanci da za su iya tayar da hankali ko kuma dagula tarbiyyar al’umma.

Daya daga cikin muhimman matsayar da aka cimma a taron shi ne cewa duk wani da zai je kafafen yada labarai sai ya sa hannu kan takardar yarjejeniyar kauce wa furuci cin mutunci, kage ko saba wa al’adun jama’a. Haka kuma an gargadi masu gabatar da shirye-shirye da su guji tambayoyin da ka iya janyo martani mai zafi ko na batanci ko tunzuri a cikin shiri.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ćłan Nijeriya sun rage fita kasashen waje neman lafiya karkashin mulkin Tinubu – Rahoton jaridar Punch

Babban bankin Nijeriya, CBN ya bayyana cewa ’yan Nijeriya sun kashe dala miliyan 4.74 wajen neman lafiya a kasashen waje daga Mayu 2023 zuwa Maris...

Jam’iyyar PDP reshen Arewa maso Yamma ta nesanta kanta da Tanimu Turaki a matsayin dan takarar shugabancin jam’iyyar daga yankin

Jiga-jigan jam’iyyar PDP daga yankin Arewa maso Yamma sun nesanta kansu daga amincewar da aka yi da tsohon ministan ayyuka na musamman, Tanimu Turaki, SAN,...

Mafi Shahara