Fadar shugaban kasa ta fara aiwatar da tsarin biyan basussukan da kamfanonin samar da wutar lantarki ke bin ta da ya kai Naira tiriliyan 2, nan da karshen rubu’i mai zuwa, a wani bangare na kokarin daidaita harkar wutar lantarki a Nijeriya.
Wakilin mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin makamashi Eriye Onagoruwa ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a wajen taron masu ruwa da tsaki na harkar samar da wutar lantarki karo na biyu na shekarar 2025, wanda hukumar kula da wutar lantarki ta Nijeriya ta shirya.
Onagoruwa ya ce fadar shugaban kasa na son magance matsalar bashin da ya kawo cikas ga kamfanonin samar da lantarki wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata.
