DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Har yanzu Nijeriya laluben shugabanni nagari take yi – Sheikh Gumi

-

Sheikh Gumi

Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Mahmoud Gumi, ya ce har yanzu Nijeriya na neman shugabannin da za su ciyar da kasar gaba.

A cewarsa, irin wadannan shugabanni su ne wadanda ke fifita jin dadin ‘yan kasa fiye da tara dukiya.

Malamin ya bayyana hakan ne a yayin bikin karramawa da kungiyar tsofaffin daliban makarantar Sultan Bello (SUBOPA) ta shirya domin karrama mambobinsu guda biyu Manjo Janar Abdulmalik Jibrin (Rtd) da Birgediya Janar Abdulkadir Gumi (Rtd) wanda ya samu mukamin gwamnati kwanan nan. 

Gumi ya bayyana Manjo Janar Jibrin a matsayin hafsan soja mai himma, da’a, da kuma kwazo a lokacin aikin sa, inda ya ce Nijeriya na bukatar mutane irinsa a matsayin shugabanci saboda jajircewa da kishin kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Atiku Abubakar ya caccaki hukumar EFCC kan tsare tsohon dan majalisa Gudaji Kazaure

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya soki hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, kan tsare tsohon dan...

Gwamnatocin Pakistan da Indiya sun amince da tsagaita wuta a Asabar dinnan

Ministan harkokin wajen Pakistan Ishaq Dar ya sanar a shafinsa na X cewa, kasashen sun amince da Shirin tsagaita wuta cikin gaggawa. Shugaba Trump ya sanar...

Mafi Shahara