DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Katsina ya kashe naira biliyan 5.7bn domin tallafawa kiwon awaki ga mata 3,610

-

 

Google search engine

Gwamnatin jihar Katsina ta kashe naira biliyan 5.4 don tallafa wa mata 3,610 su yi kiwon awaki a fadin jihar, kowacce ta samu akuya hudu.

Gwamna Dikko Radda ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da rabon tallafin a karkashin shirin kiwon akuya a Dan Nakolo da ke karamar hukumar Daura.

Gwamnan ya bayyana cewa wannan bikin wani gagarumin ci gaba ne a harkar noma a jihar, kuma wani mataki ne na tabbatar da aniyar ganin jihar Katsina ta zama jagora a fannin dogaro da kai a fadin yankin Arewa da Nijeriya baki daya. 

A cewarsa, shirin bayar da akuyoyin wani muhimmin bangare ne na dabarun bunkasa kiwon dabbobi, da inganta samar da abinci da samar da dama mai dorewa ga manoma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ana zargin hannun wani tsohon gwamna daga Kudancin Nijeriya a shirin juyin Mulki

Rahotanni sun bayyana cewa ana bincikar tsohon gwamnan ɗaya daga jihohin kudu bisa zargin cewa yana da alaƙa da wasu jami’an soji 16 da aka...

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar. Yahaya Bello...

Mafi Shahara