DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Katsina ya kashe naira biliyan 5.7bn domin tallafawa kiwon awaki ga mata 3,610

-

 

Google search engine

Gwamnatin jihar Katsina ta kashe naira biliyan 5.4 don tallafa wa mata 3,610 su yi kiwon awaki a fadin jihar, kowacce ta samu akuya hudu.

Gwamna Dikko Radda ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da rabon tallafin a karkashin shirin kiwon akuya a Dan Nakolo da ke karamar hukumar Daura.

Gwamnan ya bayyana cewa wannan bikin wani gagarumin ci gaba ne a harkar noma a jihar, kuma wani mataki ne na tabbatar da aniyar ganin jihar Katsina ta zama jagora a fannin dogaro da kai a fadin yankin Arewa da Nijeriya baki daya. 

A cewarsa, shirin bayar da akuyoyin wani muhimmin bangare ne na dabarun bunkasa kiwon dabbobi, da inganta samar da abinci da samar da dama mai dorewa ga manoma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gasar cin kofin kasashen nahiyar Afirka AFCON za ta koma duk bayan shekaru 4 – CAF

Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF, ta sanar da cewa gasar cin kofin kasashen Afrika AFCON, za ta koma duk bayan shekara huÉ—u bayan...

Tinubu ya ziyarci jihar Borno domin bude ayyuka

Shugaba Tinubu, ya ziyarci Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, domin ƙaddamar da manyan ayyuka da halartar bikin auren ɗan tsohon gwamnan jihar, Sanata Ali Modu...

Mafi Shahara