Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuGwamnonin APC sun sake jaddada bukatar kafa 'yan sandan jihohi

Gwamnonin APC sun sake jaddada bukatar kafa ‘yan sandan jihohi

Dandalin gwamnonin jam’iyyar APC ta goyi bayan kafa ‘yan sandan jihohi kamar yadda gwamnan jihar Benue Hyacinth Alia ya bayar da shawara.

Kungiyar ta kuma yi alkawarin goyon bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, a yunkurinsa na tunkarar kalubalen tsaron kasar nan.

Kungiyar ta bukaci gwamnoni da su kare jihohinsu ta hanyar amfani da jami’an tsaron al’umma.

Bayan ganawar sirri ta sa’o’i uku da suka yi, shugaban dandalin kuma gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma ya shaidawa manema labarai a Abuja cewa gwamnonin na duba batun samar da ‘yan sandan jihohi ne bisa shawarar gwamnan Benue.

Wannan na zuwa ne yayin da kungiyar gwamnonin Nijeriya suka yi wani taron gaggawa a Abuja kan kalubalen matsalar tsaron kasar.

Duk da cewa ba a bayyana ajandar taron ba, an ga mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Mallam Nuhu Ribadu, da ministan tsaro Mohammed Badaru a wurin taron.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata