Fadar shugaban Nijeriya ta ce Shugaba Tinubu zai zabi wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben shugaban kasa na 2027, bayan ya amince da takarar jam’iyyar a lokacin babban taronta a 2026.
Mashawarci na musamman ga shugaban kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga, ya bayyana hakan a ranar Alhamis a wata tattaunawa ta musamman da ya yi da jaridar Daily Trust.
Da yake amsa tambaya kan dalilin da ya sa fadar shugaban kasa ta yi shiru yayin da ake ci gaba da samun cece-kuce kan batun cire mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima daga takarar Tinubu, Onanuga ya yi watsi da ikirarin cewa sun yi shiru ne saboda sun amince a sauya mataimakin shugaban kasar.
