DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Bola Tinubu ya amince da a kashe naira biliyan 80 wajen fadada madatsar ruwa ta Alau a jihar Borno

-

 

Shugaba Tinubu

Google search engine

Ministan albarkatun ruwa Farfesa Joseph Utsev, ne ya tabbatar da hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan taron majalisar zartaswa ta kasa FEC a ranar Talata.

Utsev, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin ma’aikatun da ke kula da madatsun ruwa, ya bayyana cewa shugaban kasar ya amince da gyaran madatsar ruwa ta Alau, bayan tattaunawa da aka yi bisa bukatar hakan.

Kwamitin, wanda aka kafa a ranar 23 ga Satumba, 2024, ya hada da ministocin kudi, muhalli, ayyuka, yada labarai, da kuma mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro a matsayin mambobi.

An kaddamar da kwamitin ne a ranar 2 ga Oktoba, 2024 da nufin tantance madatsun ruwa a fadin kasar tare da ba da shawarar ingantasu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

El-Rufai ya nemi Ribadu ya yi karin haske kan ‘gubar’ thallium sulphate mai matukar hatsari

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bukaci Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara Kan harkokin tsaro Malam Nuhu Ribadu, da ya fayyace rahotannin...

Hadin kan siyasa na karuwa a Kano – Gwaman Kano

Gwamnan Kano State, Abba Kabir Yusuf, ya ce ana samun ci gaba a hadin kan siyasa a jihar, yana mai fatan rikicin masarautar Kano zai...

Mafi Shahara