DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ba zai iya cin zaben 2027 da tsauraran manufofin sa ba – Shugaban jam’iyyar SDP Gabam

-

 

SDP Chiarman Gabam

Google search engine

Shugaban jam’iyyar SDP a Nijeriya, Shehu Gabam, ya ce tsauraran manufofin tattalin arzikin shugaban Bola Tinubu na iya zama babbar matsala a gare shi idan ya yi yunkurin sake tsayawa zabe a 2027.

Gabam da yake lissafo wasu daga cikin manufofin gwamnatin Tinubu a gidan talabijin na Channels, ya ce cire tallafin man fetur,karin kudin wutan lantarki, da karin kudin sadarwa na daga cikin abubuwanda ka iya ba shi matsala.

Ya kara da cewa Tinubu na bukatar ya sake duba wasu daga cikin manufofinsa, da bukatar ya sauya majalisar ministocinsa idan yana son ya ci zabe domin ba zai iya cin baze da irin wadannan manufofin ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma 32 a jihar Niger

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar...

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Mafi Shahara