Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuKa fita ka ga yadda matsalar rashin tsaro take, ba sauraren karairayin...

Ka fita ka ga yadda matsalar rashin tsaro take, ba sauraren karairayin gwamnoni ba – Kiran Jam’iyyar ADC ga Shugaba Tinubu

Jam’iyyar hadaka ta ADC mai adawa a Nijeriya, ta bayyana cewa gwamnoni na yi wa Shugaba Bola Tinubu karya game da matsalar tsaro da ke addabar kasar, tana mai ba da shawarar cewa lokaci ya yi da shugaban zai fita ya duba halin da ‘yan ƙasa ke ciki a tituna da ƙauyuka.

Jam’iyyar ta ce, akasin ikirarin da wasu jami’an gwamnatin Tinubu ke yi, musamman mai magana da yawun shugaban ƙasa Daniel Bwala, matsalar rashin tsaro har yanzu na cigaba da ci gaba a sassan ƙasar, musamman yankunan da ke fama da hare-hare, garkuwa da mutane da fashi da makami.

Mai magana da yawun ADC Bolaji Abdullahi, ya bayyana cewa idan ana son mafita ta gaskiya kan rikicin tsaro, shugabanci dole ya kasance cikin jama’a ba kawai cikin rahotannin gwamnoni ba.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata