Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuWike ya ba da umarnin rufe wuraren hakar ma'adinai da aka yi...

Wike ya ba da umarnin rufe wuraren hakar ma’adinai da aka yi ba bisa ka’ida ba a Abuja

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ba da umarnin rufe ayyukan hakar ma’adanai da akeyi ba bisa ka’ida ba a cikin Abuja.

Kwamishinan ‘yan sandan Abuja, Ajao Saka Adewale, ne ya bayyana hakan a ranar Talata yayin da yake ganawa da manema labarai sakamakon taron kwamitin tsaro na babban birnin tarayya Abuja da aka gudanar a fadar gwamnatin tarayya da ke ofishin ministan wanda ministan ya jagoranta.

Kwamishinan ya ce, batun hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a kewayen birnin ya kasance abin damuwa, kuma hakan yana da illa ga tsaro da hakan yasa Ministan ya ba da umarnin a rufe duk wasu wuraren hakar ma’adanan nan take.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata