DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babban Hafsan Sojin kasa COAS, Olufemi Oluyede, ya amince da canjawa manyan hafsoshi a Nijeriya wajen aiyyu

-

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Onyema Nwachukwu, ya fitar ranar Asabar a Abuja.

Google search engine

Nwachukwu, ya bayyana cewa, sake tura sojoji wani shiri ne na inganta aiki ayyukan rundunar.

Ya ce jami’an da abin ya shafa sun hada da kwamandojin rundunar, manyan hafsoshi, manyan kwamandojin (GOC), kwamandojin cibiyoyin horar da sojoji, birgediya da sauran manyan mukamai.

 A cewarsa, sake tura dakarun da kuma sauyawa wasu wuraren aiki na nuni da kudurin rundunar na tabbatar da tsarin jagoranci da zai iya magance matsalolin tsaro a fadin kasar.

Mista Nwachukwu ya ce wasu daga cikin manyan hafsoshin da aka canza wa wajen a hedkwatar sojojin sun hada da Manjo Janar Lawrence Fejokwu, daga Kwalejin Tsaro ta kasa zuwa sashin kula da harkokin soji, wanda aka nada shi Shugaban Gudanarwa na rundunar Soji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara