Jam’iyyar NNPP reshen jihar Kano ta sanar da kori ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji, Abdulmumin Jibrin Kofa, bisa zargin ayyukan da suka saba wa jam’iyya da kuma kasa cika wajibin kuɗaɗen da ya rataya a wuyansa ga jam’iyyar.
Shugaban NNPP a Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa, wanda ya bayyana haka yayin jawabi ga manema labarai a Kano ranar Asabar, ya ce matakin ya biyo bayan kalaman da Jibrin ke yi a kafofin watsa labarai kan jam’iyyar da shugabanninta.
Daily Trust ta ruwaito cewa wannan lamari ya faru ne cikin sa’o’i 24 bayan ɗan majalisar ya bayyana cewa bai kamata a yi mamaki ba idan ya fice daga jam’iyyar.
Ya kuma ce ya isa girma don ya ɗauki matsaya da kansa kan abin da ya fi masa amfani a siyasance.
Da yake mayar da martani, Dungurawa ya bayyana Jibrin a matsayin “ɗan siyasa marar ƙarfi” wanda nasarar da ya samu a zaɓe ta faru ne kawai saboda goyon bayan tafiyar Kwankwasiyya da kuma jam’iyyar NNPP, ba wai ƙarfin kansa ba.
Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta kori Abdulmumini Jibrin Kofa
RELATED ARTICLES
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
