Yawan sojojin da ake tsare da su bisa zargin yunƙurin juyin mulki ya ƙaru zuwa 42, kamar yadda majiyoyi daga cikin rundunar sojin suka tabbatar wa jaridar Daily Trust.
Majiyoyin sun shaida wa jaridar Daily Trust cewa, har yanzu ana ci gaba da gano yadda kowannensu ya taka rawa da yadda shirin ya faro.
Majiyar ta kara da cewa hukumar leken asiri ta sojoji DIA da na ci gaba da bin diddigin lamarin,yayin adadin wadanda ake zargi ya karu daga 16, zuwa 42.
Sai dai mai bai wa shugaba Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Dare, ya ce fadar shugaban kasa na tare da matsayar rundunar tsaron kan wannan batu.
