Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedShugaban kasar Kamaru Paul Biya ya sauya manyan hafsoshin sojin kasar

Shugaban kasar Kamaru Paul Biya ya sauya manyan hafsoshin sojin kasar

Rahotanni sun tabbatar da cewa a daren Laraba ne Shugaba Paul Biya ya rattaba hannu kan wata sabuwar doka ta sauya jami’ai a makarantar tsaro ta kasar ta Kamaru (International School of Security Forces).

Sabon sauyin ya shafi sassa daban-daban na makarantar, ciki har da sashen nazari, cibiyar bincike da tattara bayanai, da kuma sashen gudanarwa.

A cikin shekara guda kacal, Shugaba Biya mai shekara 92 ya yi sauyin manyan hafsoshin soja fiye da sau shida, tun bayan shekarar 2023 lokacin da juyin mulki ya yi kamari a kasashen yankin Sahel da ma makwabciyarsu Gabon.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata