Wednesday, April 8, 2026
HomeKetareShugaban mulkin sojin Nijar na ci gaba da ziyayar aiki a kasar

Shugaban mulkin sojin Nijar na ci gaba da ziyayar aiki a kasar

Mako guda kenan da shugaban gwamnatin mulkin sojin Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya fara zagaye cikin mota a kasar

Tun a ranar Asabar 8 ga watan Nuwamba shugaba Tiani ya fara wani rangadi a cikin wadansu yankuna na jihohin kasar da ayarin motocinsa.

Shugaban na Nijar ya fara wannan zagaye ne daga jihar Dosso kafin daga bisani ya zarce Tahoua sai kuma jihar Agadez, yayin da ‘yan jihar Zinder ke dakon zuwan sa a wannan rana ta 15 ga watan Nuwamba.

Masu ruwa da tsaki dai na ganin wannan zagayen da shugaban ke yi na zama irin sa na farko da aka ga wani shugaba na yi a tarihin kasar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata