Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuGwamnan Kano ya dauki malaman lissafi 400 aiki a makarantun sakandire

Gwamnan Kano ya dauki malaman lissafi 400 aiki a makarantun sakandire

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan takardar daukar malaman lissafi 400 a makarantun sakandiren da ke fadin jihar aiki.

 

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ta bayyana cewa daukar matakin wani yunkuri ne na cike gibin da ake samu a ilimin daliban jihar Kano, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

 

A cewar sa, darasin lissafi shi ne ginshikin kimiyya, fasaha, kirkire-kirkire har ma da fagen injiniyanci, a don haka ya zama wajibi gwamnati ta mayar da hankali wajen inganta matakin iliminta.

 

Gwamnan ya bukaci sabbin malaman da su sanya kwarewa da mayar da hankali wajen ganin sun sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata