Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedMalaman makarantun boko a Nijeriya na barazanar tsunduma yajin aiki saboda yawan...

Malaman makarantun boko a Nijeriya na barazanar tsunduma yajin aiki saboda yawan satar dalibai

Kungiyar malaman makaranta ta Nijeriya NUT ta yi gargaɗin yiwuwar tsunduma yajin aiki a fadin ƙasar, bayan hare-haren makarantun Kebbi da Niger da suka yi sanadin halaka mutum biyu da sace ɗalibai da dama.

A wata sanarwa da kungiyar ta fitar ta nuna takaicinta na halaka mataimakin shugaban makaranta da jami’in tsaron da ke kula da makarantar, da kuma sace dalibai 25 a jihar Kebbi.

Haka kuma ta yi Allah wadai da sace sama da dalibai 300 da ma’aikata 12 a jihar Niger, tana mai kiran wadannan hare-haren da ta’addanci kuma abin ƙyama.

NUT ta ce dole gwamnati ta ɗauki mataki cikin gaggawa domin dakile sake faruwar irin wadannan hare-haren, domin a cewarta, hakan na iya jefa tsarin ilimi cikin halaka.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata