Tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilan Nijeriya Hon. Idris Wase, ya roƙi shugaba Tinubu da ya sake duba umarnin da ya bayar na janye ’yan sanda daga tsaron manyan mutane, domin ‘yan bindiga na yi musu barazana.
A lokacin da Majalisar ke tsaka da muhawara a Larabar nan Wase ya yi wannan bayani, yana mai jaddada cewa akwai bukatar shugaban ya fayyace rukunin manyan mutane da janyewar ta shafa.
Wannan korafin na zuwa ne bayan Tinubu ya bada umarni a Abuja ranar Lahadi, lokacin taron tsaro tare da hafsoshin tsaro da daraktan hukumar DSS.
