Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuSheikh Dahiru Bauchi ya rasu 

Sheikh Dahiru Bauchi ya rasu 

Sheikh Dahiru Bauchi ya rasu kamar yadda daya daga cikin ‘ya’yansa ya tabbatar wa da DCL Hausa. Ya shaida mana cewa fitaccen malamin addinin ya rasu ne a safiyar Alhamis din nan a garin Bauchi

Allah ya albarkaci Sheikh Dahiru Bauchi da ‘ya’ya da dama. Khalid Abdullahi Zaria wanda ya rubuta littafi na musamman kan rayuwar malamin ya ce Sheikh Dahiru Bauchi na da ‘ya’ya 95, 48 daga cikinsu mata ne. A cikinsu guda 77 sun haddace Qur’ani.

An haifi fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ke jagorantar Darikar Tijjaniyya a Najeriya, da ake hasashen shekarunsa sun haura 100 kafin Allah Ya karbi rayuwarsa. Tuni wannan labari ya jefa gaba daya duniyar Musulunci a Nijeriya da suaran kasashen Afirka ta yammam musamman mabiyansa, almajiransa, da ‘yan uwa cikin jimami.

Tun yana karamin yaro ya fara karatun Alƙur’ani karkashin jagorancin mahaifinsa, Alhaji Usman Adam, har ya haddace Qur’ani Mai Tsarki kafin ya girma.

Sheikh Dahiru Bauchi ya yi karatu a wajen malamai irinsu Sheikh Usman Zangon Barebari, Sheikh Abdulkadir Zaria, da Sheikh Abubakar Atiku — sannan daga baya ya karbi Darikar Tijjaniyya tare da zurfafa iliminsa a fannin tafsiri, hadisi.

Sheikh Bauchi ya kwashe shekaru da dama yana gudanar da tafsirin Alƙur’ani — a zahiri tun wajen shekarun 1950, jim kadan bayan da ya yi auren fari a 1948.

Karfin iliminsa da tasirinsa a darikar Tijjaniya ya sa ya yi nasarar samar da mutane fiye da 140,000 da suka haddace Qur’ani a cibiyoyin da ya gina a Nijeriya da sauran kasashe, a cewar rahoton Daily Trust da aka wallafa a shekarar 2022.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata