Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuADC ta nesanta kanta da Nasiru El-Rufa’i bayan taron jam'iyyar da aka...

ADC ta nesanta kanta da Nasiru El-Rufa’i bayan taron jam’iyyar da aka yi tashin hankali a Kaduna

Rikicin siyasa na ƙara kamari a jihar Kaduna bayan jam’iyyar ADC ta nesanta kanta daga wani taron da aka danganta da tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufa’i, a daidai lokacin da rundunar ‘yan sanda ta fara bincike kan zarge-zargen tashin hankali da harbe-harbe a wajen taron.

A wata sanarwa da mai magana da yawun ADC na jihar Kaduna, Injiniya Musa Idris, ya sanya wa hannu a ranar Asabar, jam’iyyar ta karyata abin da aka kira kwamitin wadanda suka sauya sheka daga APC, PDP, SDP, LP, NNPP zuwa ADC, da aka ƙaddamarwa.

Jam’iyyar ta jaddada cewa El-Rufa’i ba ɗan ADC bane, don haka bai da wani hurumin shirya taruka a madadinta.

A gefe guda kuma, rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta tabbatar da cewa ta fara binciken lamarin bayan samun rahoton cewa ‘yan daba sun yi ɓarna a wajen taron siyasar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata