Hamshaƙin ɗan kasuwa a Najeriya Aliko Dangote yayi zargin cewa ana shigo da Bara gurbin mai zuwa ƙasarnan a saidawa ‘yan Najeriya.
A yayin wata ziyara da kakakin majalisar wakilai ta taraiya Tajuddeen Abbas ya jagoranci ‘yan majalisar zuwa matatar mai ta Dangote, Aliko Ɗangwate ya fada musu cewa akwai bukatar gudanar da bincike saboda gani ko akwai masu zagon ƙasa ga harkar mai ko ma ga harkar kasuwancin shi.
Ya bada shawarar a riƙa bi gidajen mai ana duba man da ake sayar wa ‘yan Najeriya dan tabbatar da hakan.
Dangote ya ƙalubalanci shugaban hukumar kula da harkokin haƙo tare da tãce man fetur na ƙasar Ahmed Farouk kan ingancin man da ake tãce wa a gida, inda ya ce man da da yake tãce yafi wanda ake shigo da shi nesa ba kusa ba.
Kakakin majalisar wakilai ta Najeriya Tajuddeen Abbas ya ce la’akari da zarge zarge da bangarorin biyu ke yi akwai bukatar gudanar da bincike.

