Tuesday, April 7, 2026
HomeBabban LabarinmuAmurka ta yabawa gwamnatin Nijeriya bayan kaddamar da hari

Amurka ta yabawa gwamnatin Nijeriya bayan kaddamar da hari

Sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya bayyana godiyarsa ga gwamnatin Najeriya bisa goyon bayan da ta bayar a yayin farmakin sama da aka kai kan sansanonin ‘yan ta’adda a yankin Arewa maso Yamma.

 

Wannan na zuwa ne bayan rahotannin da suka ce Amurka ta kaddamar da babban farmakin soji kan kungiyoyin ta’addanci a ranar Alhamis.

 

A cewar wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta fitar, an kai hare-haren ne a matsayin wani ɓangare na haɗin gwiwar tsaro tsakanin Najeriya da ƙasashe abokanta, ciki har da Amurka domin dakile barazanar ta’addanci da tsattsauran ra’ayi.

 

Sanarwar ta jaddada cewa ana aiwatar da dukkan matakan yaki da ta’addanci ne bisa kare rayukan fararen hula, mutunta ikon ƙasa, da tabbatar da tsaro da hadin kan al’umma ba tare da nuna bambancin addini ko kabila ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata