Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuAn fadi dalilin da ya sa dan sandan da ke yi wa...

An fadi dalilin da ya sa dan sandan da ke yi wa Ganduje dogari ya sunkuya ya daura masa takalma a kafa

Mataimaki na Musamman ga shugaban jam’iyyar APC na kasa, kan harkokin sadarwa Aminu Dahiru Ahmad, ya kare dan sanda da aka gani yana daura wa shugaban jam’iyya takalmi.

Bidiyon da ya nuna dan sandan a duke gaban Ganduje yana daura masa takalmi ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Aminu Dahiru Ahmad ya ce shaidun gani da ido sun tabbatar cewa dan sandan ya kai dauki ga takalman Ganduje ne domin tabbatar da tsaron lafiyarsa.

Ya ce sabanin abin da wasu ke yayatawa, Ganduje yana girmama masu taimaka masa da ma’aikatan gidansa matuka.

Aminu Dahiru ya ce, wannan gajeren bidiyo dai shaida ce da ke nuna yadda kyakkyawar alaka take tsakanin Dr Abdullahi Umar Ganduje da masu taimaka masa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata