An kama wasu malaman bogi a jami’ar Bayero dake Kano
Jami’an tsaro na jami’ar Bayero Kano (BUK) sun kama wasu mutane biyu da suke bayyana a matsayin malamai da kuma sayar da littattafai ga daliban a makarantar.
A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin magatakardan makarantar Bala G. Abdullahi ya fitar ya rabawa manema labarai tace wadanda ake zargin, Mista David Iluebe da Mista Chike E. Eke daga jihohin Edo da Delta, sun shiga wani dakin karatu a Kwalejin Injiniyan ci jami’ar.
Suka gabatar da kansu a matsayin malamai kuma sun gabatar da jerin litattafai guda huɗu da suka shafi batutuwa kamar Ingilishi, Ƙididdiga, Jama’ar Nijeriya da Al’adu-a matsayin wajibi ga dalibai’ wanda zasu zaman musu Continuous Assessment (C.A.).
Rahotanni sun ce sun yi barazanar cewa rashin sayen littattafan zai sa su kasa cin kwasa kwasan da malaman zasu dauke su.
Mukaddashin magatakardar ya bayyana cewa dalibai, sun damu da biyan sossai kuma sun sayi littattafan. Sai dai abin nasu ya janyo surutu, wanda ya kai ga cafke su da jami’an tsaron jami’ar suka yi bayan wani korafi da suka samu. Yanzu haka dai mutanen biyu suna fuskantar tuhuma kan aikata laifuka, damfara, da kuma zamba.
Binciken farko ya nuna cewa wadanda ake zargin sun yi ikirarin su ne suka wallafa littattafan da suke sayarwa.
Sun amince da zargin kuma sun bayyana cewa suna yin wannan makirci ne saboda rashin aikin yi, wadanda ake zargin sun kuma bayyana cewa wannan shi ne yunkurinsu na biyu a jihar Kano, inda a baya suka yi aiki a kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar Kano a farkon wannan shekarar.

