Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedAn rubuta wa majalisar dokokin Kano wasikar neman a rusa masarautu 4,...

An rubuta wa majalisar dokokin Kano wasikar neman a rusa masarautu 4, a dawo da guda daya

 An rubuta wa majalisar dokokin Kano wasikar neman a rusa masarautu 4, a dawo da guda daya

Wata kungiya mai suna “Yan Dangwalen Jihar Kano” (The Kano Electorate), ta rubuta wa majalisar dokokin jihar Kano takardar neman a sake duba dokar kafa karin masarautu hudu na Gaya, Rano, Karaye da Bichi da gwamnatin Ganduje ta yi.

A wata wasika mai dauke da kwanan watan 5 ga Fabrairu, 2024 da aka aika wa kakakin majalisar dokokin jihar Kano ta nemi a rusa masarautun tare da maido da Muhammad Sanusi II a matsayin Sarkin Kano, inda kungiyar ra ce hakan zai samar da hadin kai da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Kano da kuma makwabtanta a cewar wasikar. 

A ranar 5 ga watan Disamba, Shekarar 2019, tsohon gwamnan jihar Abdullahi Ganduje ya rattaba hannu kan dokar masarautu kuma a nan take majalisar dokokin ta amince da dokar. 

 Jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa ana ta cece-kuce kan shirin mayar da Sarki Muhammadu Sunusi ll, kan karagar mulki tare da rusa sauran. masarautun wadanda ake tunanin an kirkire su ne domin tozarta tsohon Sarkin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata