Kotun Tarayya da ke Kaduna ta sanya ranar 14 ga watan Afrilu, 2026 domin yanke hukunci kan bukatar beli da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya gabatar.
A yau Laraba ne lauyoyin El-Rufa’i wanda ake kara da kuma masu gabatar da kara wato ICPC suka gabatar da hujjojinsu a gaban kotun da ke Kaduna domin duba batun bukatar ba da tsohon gwamnan na jihar Kaduna beli.
Babban lauyan masu kare El-Rufai, Adewole Iyamu, ya bayyana cewa suna da kwarin gwiwar samun sakamako mai kyau, yana mai cewa sun gabatar da dukkan hujjojinsu yadda ya kamata a gaban kotu.
Iyamu ya tabbatar da cewa an gabatar da bukatar belin a hukumance, kuma bangaren masu kara sun mayar da martani akan bukatar.
Haka kuma, ya ce ana sa ran El-Rufai zai gurfana a gaban Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar 10 ga watan Afrilu kan wata kara daban da Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS) ta shigar.
A cewarsa, bangaren wanda ake kara sun kammala dukkan shirye-shiryen da suka dace domin sauraron karar ranar 10 ga Afrilu, inda ya ce sun riga sun shigar da dukkan takardun da ake bukata.
