DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Saturday, April 18, 2026
HomeSiyasaAn saka ranar 14 ga Afrilu don yanke hukunci kan bukatar ba...

An saka ranar 14 ga Afrilu don yanke hukunci kan bukatar ba da belin El-Rufai

Kotun Tarayya da ke Kaduna ta sanya ranar 14 ga watan Afrilu, 2026 domin yanke hukunci kan bukatar beli da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya gabatar.

A yau Laraba ne lauyoyin El-Rufa’i wanda ake kara da kuma masu gabatar da kara wato ICPC suka gabatar da hujjojinsu a gaban kotun da ke Kaduna domin duba batun bukatar ba da tsohon gwamnan na jihar Kaduna beli.

Babban lauyan masu kare El-Rufai, Adewole Iyamu, ya bayyana cewa suna da kwarin gwiwar samun sakamako mai kyau, yana mai cewa sun gabatar da dukkan hujjojinsu yadda ya kamata a gaban kotu.

Iyamu ya tabbatar da cewa an gabatar da bukatar belin a hukumance, kuma bangaren masu kara sun mayar da martani akan bukatar.

Haka kuma, ya ce ana sa ran El-Rufai zai gurfana a gaban Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar 10 ga watan Afrilu kan wata kara daban da Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS) ta shigar.

A cewarsa, bangaren wanda ake kara sun kammala dukkan shirye-shiryen da suka dace domin sauraron karar ranar 10 ga Afrilu, inda ya ce sun riga sun shigar da dukkan takardun da ake bukata.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata