Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuAn tilasta wa IGP Kayode Egbetokun yin murabus daga mukaminsa - Premium...

An tilasta wa IGP Kayode Egbetokun yin murabus daga mukaminsa – Premium times

Rahotanni na nuni da cewa an tilasta wa Sufeto Janar na ‘yan Sandan Nijeriya, Kayode Egbetokun, yin murabus daga muƙaminsa bisa umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, kamar yadda majiyoyi daga fadar shugaban ƙasar suka tabbatar.

Jaridar Premium times ta rawaito cewa majiyar ta ce an bukaci Egbetokun ya ajiye muƙaminsa ne a wani taro da aka yi da shugaban ƙasa a fadarsa a ranar Litinin.

An kuma bayyana cewa ana shirin nada mataimakin Sufeto Janar na ‘yan Sanda AIG, Tunji Disu, domin maye gurbinsa, amma har zuwa lokacin kammala wannan rahoto ba a fitar da sanarwar nadin nasa a hukumance ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata