Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuAtiku Abubakar ya caccaki hukumar EFCC kan tsare tsohon dan majalisa Gudaji...

Atiku Abubakar ya caccaki hukumar EFCC kan tsare tsohon dan majalisa Gudaji Kazaure

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya soki hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, kan tsare tsohon dan majalisar wakilai Muhammad Gudaji Kazaure.

A cikin sakon da ya wallafa a shafinsa na X jigo a jam’iyyar PDP ya bayyana tsare Kazaure a matsayin rashin bin doka da oda ne, ta hanyar kamawa da tsare ‘yan kasa ba tare da bin ka’ida ba.

Ya ba da misali da batun VeryDarkMan, wanda ya ce an sake shi ne bayan da jama’a suka nuna rashin jin dadinsu akan kama shi.

Atiku ya ce tun bayan kama tsohon dan majalisar a Kano aka garzaya da shi Abuja, har yanzu ba a gabatar da wata tuhuma ko yi wa iyalansa da lauyoyinsa da kuma al’ummar Najeriya karin bayani.

RELATED ARTICLES

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata