Thursday, April 9, 2026
HomeUncategorizedAtiku Abubakar ya yi ganawar sirri da Obasanjo

Atiku Abubakar ya yi ganawar sirri da Obasanjo

 

 Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya yi wata ganawar sirri da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo a birnin Abeokuta na jihar Ogun.

Ayarin motocin Atiku sun isa dakin karatu na Olusegun Obasanjo a Abeokuta, da misalin karfe 12:36 na ranar Litinin din nan.

Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ya samu tarba daga abokin Obasanjo, Otunba Oyewole Fasawe.

A cikin tawagar Atiku Abubakar din akwai, tsoffin gwamnonin jihohin Cross River da Sokoto, Liyel Imoke, Sanata Aminu Tambuwal da Sanata mai wakiltar Bauchi ta tsakiya, Abdul Ningi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata