Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya jaddada cewa babu ci-gaba a kowace al’umma idan ba a gina mulki kan doka, adalci da gaskiya ba.
Gwamnan ya faɗi haka a yayin taron karramawa na CREED, inda aka ba shi lambar yabo ta Gwamnan Shekara.
A madadinsa, Babban Lauyan Jihar Kano, Abdulkarim Maude (SAN), ya ce gwamnatinsu ta gudanar da gyare-gyare domin rage jinkirin shari’a da matsalolin tsare-tsaren da suka daɗe ba tare da gurfanarwa ba.
Haka kuma ya bayyana cewa an gano wasu mutane da suka shafe shekaru a tsare ba tare da fayil ko lauya ba, lamarin da ya sa gwamnan ya umarci a nemo takardun, a gaggauta shawarwarin shari’a, a gurfanar da inda ya dace, ko a janye inda adalci ya buƙaci hakan.
Gwamnan ya ce ana faɗaɗa taimakon shari’a da haɗa masu aiki na sa-kai don tabbatar da cewa adalci bai taɓa dogaro da kuɗi ko matsayi ba. Manufarsa ita ce ganin tsarin shari’a ya zama mai sauƙin samu, ingantacce kuma adalci ga kowa kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
