Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuBai kamata a nuna sakin yaran da aka sace a matsayin nasara...

Bai kamata a nuna sakin yaran da aka sace a matsayin nasara ga gwamnati ba – Atiku Abubakar

Madugun adawa a Nijeriya Atiku Abubakar, ya soki gwamnatin tarayya kan hanyar da aka bi wajen sakin ‘yan matan da aka sace a Kebbi, yana mai cewa bai kamata a nuna shi a matsayin nasara ba, illa hakan na nuna tabarbarewar lamarin tsaron kasar.

A wata sanarwa da ofishin yada labaran Atiku ya fitar a ranar Laraba, ya ce babban abin damuwa shi ne yadda ‘yan ta’adda a halin yanzu ke yawo babu tsoro, suna tattaunawa, suna kuma sa dokoki da suke so a bi.

A wata sanarwa da mai bai wa shugaban Tinubu shawara kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fitar, ya bayyana cewa DSS da sojoji sun bibiyi ‘yan bindigar kai tsaye a lokacin harin, har suka samu damar tattaunawa da su don a sako daliban ba tare da biyan kudin fansa ba.

Sai dai Atiku ya bayyana wannan magana a matsayin kokarin rufe bakin jama’a da kuma juya gazawar gwamnati ta koma nasara.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata