Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedBirtaniya da Faransa na duba yiwuwar haramta wa yara amfani da kafafen...

Birtaniya da Faransa na duba yiwuwar haramta wa yara amfani da kafafen sada zumunta

Kasashen Faransa da Birtaniya na duba yiwuwar bin sahun Australia wajen hana yara da matasan da suka gaza shekaru 20 da haihuwa amfani da kafafen sada zumunta, sakamakon damuwa kan tabarbarewar lafiyar kwakwalwa a tsakanin matasa.

Rahoton ya nuna cewa Australia ita ce ƙasa ta farko da ta haramta wa ’yan ƙasa da shekaru 16 amfani da kafafen sada zumunta kamar Instagram, Facebook, TikTok da YouTube, matakin da ya janyo muhawara a duniya.

A Faransa kuwa, ana muhawara kan kudurori da ke neman hana ’yan ƙasa da shekaru 15 amfani da kafafen sada zumunta, ciki har da wanda Shugaba Emmanuel Macron ke goyon baya.

Kazalika a Birtaniya ma, masana da jami’an gwamnati na tattaunawa kan irin wannan mataki, inda aka gayyaci Jonathan Haidt, fitaccen masanin ilimin halayyar ɗan Adam daga Amurka, domin tattaunawa da jami’an gwamnatin kasar kan lamarin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata