Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuBirtaniya za ta rufe wasu hanyoyin jiragen sama da kuma tituna, baya...

Birtaniya za ta rufe wasu hanyoyin jiragen sama da kuma tituna, baya ga girke jami’an tsaro don tarbar shugaban Nijeriya Bola Tinubu a mako mai zuwa

Mahukunta a Burtaniya sun sanar da tsauraran matakan tsaro a garin Windsor yayin da Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, zai kai ziyara ta musamman a mako mai zuwa bisa gayyatar Sarkin Birtaniya, King Charles III.

‘Yan sandan Thames Valley sun ce za a kara takaita zirga-zirgar jiragen sama a sararin samaniyar Windsor daga karfe 7 na safe zuwa karfe 11:59 na dare a ranar 18 ga Maris, yayin da za a tura jami’an tsaro da suka hada da masu makamai, rundunar doki da jami’an kula da hanyoyi.

Hukumomin sun ce za a kuma yi amfani da na’urorin CCTV, katangar tsaro da sauran matakai domin tabbatar da tsaron ziyarar da za a yi a Windsor Castle, tare da gargadin cewa duk wanda ya karya dokar hana zirga-zirgar jiragen sama zai fuskanci hukunci.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata