Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedBola Tinubu ya nada shugaban hukumar kula da ayyukan 'yan sanda

Bola Tinubu ya nada shugaban hukumar kula da ayyukan ‘yan sanda

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya sanar da nadin DIG Hashimu Argungu (Rtd) a matsayin shugaban hukumar kula da ayyukan ‘yan sanda wato ‘Police Service Commission’.
Kazalika, shugaban kasar ya kuma amince da nadin Chief Onyemuche Nnamani a matsayin Sakataren hukumar da kuma DIG Taiwo Lukanu (Rtd) a matsayin mamba a hukumar.
Bugu da kari, shugaban kasar ya kuma amince da nadin Mohammed Seidu a matsayin shugaban asusun tallafa wa ‘yan sanda na ‘Police Trust Fund’.
Wadannan nade-nade na a cikin wata sanarwa daga mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai Mr Ajuri Ngelale da DCL Hausa ta samu kwafi.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata