Wednesday, April 8, 2026
HomeUncategorizedDaliban wata makarantar Sakandare sun zane malaminsu

Daliban wata makarantar Sakandare sun zane malaminsu

Wasu daliban makarantar sakandire su goma a jihar Ogun sun lakada wa wani malaminsu, Kolawole Shonuga dukan tsiya saboda ya hana daya daga cikinsu satar amsa a lokacin da suke rubuta jarabawa.
Majiyar DCLHausa ta jaridar PUNCH ta ce lamarin ya faru ne a ranar Talatar da ta gabata a makarantar Isanbi Comprehensive High School da ke Ilisan-Remo a karamar hukumar Ikenne a jihar.
A cewar jaridar malamin mai suna Shonuga, a yayin da yake tsaron jarabawar a ajin daliban SS 1, ya kama wani matashi mai suna Ashimi Adebanjo mai shekaru 18 da haihuwa, yana satar amsa inda nan take ya kwace takardarsa.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata