Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a Yammacin Afirka

ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a Yammacin Afirka

Kungiyar ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a yankin Yammacin Afirka, sakamakon ƙarin tabarbarewar tsaro da kuma yawaitar juyin mulki a wasu ƙasashen mamba.

Shugaban Hukumar ECOWAS, Omar Touray, ne ya bayyana hakan a ranar Talata yayin zaman kwamitin sulhu na majalisar karo na 55 na matakin ministoci da aka gudanar a Abuja.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa Touray ya ce halin da ake ciki ya nuna buƙatar yin nazari mai zurfi kan makomar dimokuraɗiyya a yankin, tare da ƙara zuba jari a fannin tsaro don kare al’ummomin ƙasashe mambobin kungiyar.

Majiyar DCL Hausa ta ruwaito cewa taron ya gudana ne a daidai lokacin da ake fama da juyin mulki a Guinea-Bissau, Mali, Burkina Faso da Nijar, tare da ƙoƙarin kifar da gwamnati a Jamhuriyar Benin da wasu sassan yankin, lamarin da ya ƙara tayar da hankalin shugabanni.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata