Shugaba Tinubu ya bukaci majalisa ta sahale masa nada sabbin shugabannin hukumomin kula da man fetur bayan da Injiniya Farouk Ahmed, ya yi murabus a matsayin shugaban Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Nijeriya, tare da takwaransa Gbenga Komolafe, shugaban Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Sama (NUPRC).
Dukkaninsu tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya nada su a shekarar 2021, bayan kafa hukumomin karkashin Dokar Man Fetur ta PIA.
Wannan na zuwa ne bayan zargin da attajirin dan kasuwa Aliko Dangote ya yi wa Farouk Ahmed, na rayuwa fiye da karfin albashin ma’aikacin gwamnati, musamman dangane da kudaden da ake zargin ya kashe wajen karatun ’ya’yansa a kasar Switzerland.
Zargin ya haifar da muhawara Dangote ya hakikance cewa akwai bukatar bincike inda ya gabatar da korafi a gaban Hukumar ICPC.
Sai dai a cikin sanarwar ta fito ne daga Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Yada Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya ce Shugaba Tinubu ya nada Injiniya Saidu Aliyu Mohammed a matsayin shugaban NMDPRA, tare da Oritsemeyiwa Amanorisewo Eyesan a matsayin shugabar NUPRC.
Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bukaci Majalisar Dattawa ta gaggauta tantance tare da amincewa da nadin sababbin shugabannin manyan hukumomin kula da harkokin man fetur da iskar gas na kasa.
Eng Faruk Ahmad ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban hukumar NMDPRA
RELATED ARTICLES
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
