Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuFaransa ta sha alwashin tallafa wa Nijeriya a yaki da ’yan ta’adda

Faransa ta sha alwashin tallafa wa Nijeriya a yaki da ’yan ta’adda

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana cikakken goyon bayan kasarsa ga Najeriya wajen yaki da matsalar tsaro, musamman barazanar ta’addanci da ake fuskanta a Arewa.

A wani saƙo da ya wallafa a X a ranar Lahadi, Macron ya ce ya yi magana da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda ya tabbatar masa cewa Faransa za ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da gwamnatin Najeriya.

Sanarwar ta Macron na zuwa ne bayan ƙarin hare-hare da garkuwa da mutane a yankin Arewa, lamarin da ya ja hankalin ƙasashen duniya.

Najeriya na ci gaba da neman goyon bayan ƙasashen duniya, ciki har da tattaunawar da Mai bai wa Shugaban kasa shawara kan tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, ya yi da Sakataren harkokin Yaƙin Amurka, Pete Hegseth, a Pentagon domin inganta dabarun yaki da ta’addanci a Nijeriya.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata